Tinubu ya ba ma’aikatar shari’a, majalisa damar sake duba kudirin dokar haraji

Shugaban Najeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya ba ma’iakatar shari’a da majalisun tarayya damar sake nazarin kudirin dokar haraji.

Kudirin dokar ya jawo cece-kuce, musamman tsakanin shugabannin Arewa da ke zargin an shirya jawo matsala ga yankin.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris, a ranar Talata ya ce shugaban kasa ba shi da wata mummunan manufa ga wani bangare na Najeriya.

“Kamar yadda tsarin majalisa ya ba da dama, gwamnatin tarayya ta na maraba da duk wani abu da zai kawo gyara ga wasu sassan kudirin,” cewar Mohammed Idris.

Ministan ya kara da cewa saboda wannan dalili ne, shugaban kasa ya ba ma’aikatar shari’a umarni, ta yi aiki tare da majalisa wajen gyaran kudirin kafin ya zama doka.

Tinubu ya ba ma’aikatar shari’a, majalisa damar sake duba kudirin dokar haraji



Comments

Popular posts from this blog

Ortom reacts to criticisms of Gov Alia’s Benue State Civil Protection Guards

EPL: Salah overtakes Thierry Henry in all-time top goalscorer chart

Food security: Gov Zulum advocates large-scale irrigation farming in Lake Chad region