Gwamnoni sun goyi bayan kafa ƴan sandan jihohi

An samu gwamnonin Najeriya da dama sun nuna goyon bayan samar da ƴan sandan jihohi.

An fadi haka ne a taron Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa (NEC) da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranta a ranar Alhamis.

Jihohi 35 sun gabatar da matsayarsu, inda yawancin gwamnonin suka nuna goyon bayan kafa ƴan sandan jihohi.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, da ya zanta da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa ya tabbatar da haka, amma ya ce sai a taron NEC na gaba da za a yi a watan Janairu 2025, za a ɗauki matsaya a kan lamarin.

A tuna cewa, a wani taro da aka gudanar a watan Nuwamba, jihohin Kwara, Kebbi da Adamawa sun bayyana ba su gabatar da matsayarsu kan batun kafa ƴan sandan jihohi ba.

“Yau, ɗaya daga cikin batutuwan da muka tattauna a taron NEC shine kafa ƴan sandan jihohi.”

“Yau, kusan jihohi 35 sun gabatar da matsayarsu kan kafa ƴan sandan jihohi a Najeriya. Kuma zan iya cewa, bisa bayanan da muke da su, kusan dukkan jihohin suna goyon bayan kafa ƴan sandan jihohi.”

Gwamnoni sun goyi bayan kafa ƴan sandan jihohi



Comments

Popular posts from this blog

Ortom reacts to criticisms of Gov Alia’s Benue State Civil Protection Guards

EPL: Salah overtakes Thierry Henry in all-time top goalscorer chart

Nigerian military, Briech launch locally made bombs, attack drones